11-Jan-2026
09-Jan-2026
08-Jan-2026
08-Jan-2026
07-Jan-2026
07-Jan-2026
02-Jan-2026
31-Dec-2025
An bude shekarar 2025 da gasar wasannin motsa jiki ta nahiyar asiya, wadda ta gudana tsakanin ranakun 7 zuwa 14 watan Fabarairun shekarar a birnin Harbin, gasar da ta hallara ‘yan wasa sama da 1,200 daga kasashe da yankunan duniya 34, ta kuma zamo mafi tara yawan ‘yan wasan motsa jiki a tarihinta. Kasar Sin ce ta zamo ta daya a fannin samun lambobin yabo a gasar, inda ‘yan wasanta suka lashe lambobin zinari 32, da na azurfa 27 da kuma na tagulla 26, kana ‘yan wasan Sin daga Taipei da na kasar Thailand, su ma suna kan gaba wajen cimma manyan nasarori a gasar.
08-Jan-2026
Yayin da duniya ta riga ta sa kafa a sabuwar shekarar 2026, dangantakar da ke tsakanin kasar Sin da Nijeriya, har ma da sauran kasashen nahiyar Afirka baki daya ita ma ta shiga wani sabon zubi bisa kokarin da bangarorin ke yi na aiki da tsare-tsare da dabarun ci gaba a huldodinsu. Bayan shekara guda na zurfafa hadin gwiwa da kuma sabunta kuzarin huldar diflomasiyya a shekarar 2025, ga dukkan alamu bangarorin za su mayar da hankali kan ayyukan da suka shafi samar da sakamako
07-Jan-2026
Kwanan nan ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da muhimmin jawabi na murnar shiga sabuwar shekara ta 2026, inda ya ayyana muhimman nasarorin da kasarsa ta samu a shekarar da ta gabata wato 2025, tare da bayyana kyakkyawan fata a shekara ta 2026. Daya daga cikin kwararru da masanan sassan kasa da kasa da suka bayyana ra’ayoyinsu kan jawabin shugaba Xi, Farfesa Sheriff Ghali Ibrahim daga jami’ar Abuja mai sabon mukamin shugaban fannin horaswa na hukumar hana cin hanci da rashawa da sauran makamantan laifuka ta Najeriya wato ICPC, kana shugaban cibiyar binciken harkokin Sin da Afirka na zamani a Najeriya, ya ce...
06-Jan-2026
Yar' uwa ‘yar kasar Rasha mai suna Elena, tana yin balaguro akai-akai tsakanin kasashen Sin da Rasha, inda take aikin jagorantar harkokin yawon bude ido. Tun daga shekara ta 2019, ta fara bayar da bayanan yau da kullum da suke faruwa a wani karamin birnin dake kan iyaka na arewa maso gabashin kasar Sin, wato birnin Huichun a lardin Jilin ta shafukan sada zumuntarta na yanar gizo. Bidiyoyin da ta dauka game da tituna, gine-gine, yadda tsoffi Sinawa ke raye-raye a filin wasa, da kuma abinci, kula da farce, da ra’ayoyinta na sayayya, da kuma sauran abubuwan da ke nuna rayuwar yau da kullum ta kasar Sin, sun ja hankalin mabiyanta da yawa daga kasashe daban daban.
05-Jan-2026