16-Apr-2026
16-Apr-2026
15-Apr-2026
14-Apr-2026
13-Apr-2026
11-Apr-2026
09-Apr-2026
08-Apr-2026
Yayin da gasar cin kofin kwallon kafa na duniya wadda hukumar FIFA ke shiryawa take kara karatowa, ita ma gasar kwallon kafa ta ‘yan wasa da ba kwararru ba ta kasar Sin, ko "Su Super League", ta yi matukar jan hankalin sassan duniya. ‘Yan wasa masu fafatawa a gasar, da ‘yan kallo na ta halartar filayen wasa domin nishadantuwa daga wannan gasa mai samun karin farin jini. Yayin da a gefe guda gasar ta "Su Super League" ke kara fadada sayayya, da hada-hadar kasuwanci a yankunan da ake gudanar da ita.
16-Apr-2026
A watan Maris na shekara ta 2026, wata likita 'yar kasar Sin daga birnin Nanchang na lardin Jiangxi dake kudu maso gabashin kasar mai suna Hu Minhua, wadda ta kware a fagen yaki da cutar kanjamau, ta samu lambar yabo ta fitacciyar mace ta kasa. Hu Minhua, ta shafe shekaru 26 tana jajircewa a fannin kandagarki da maganin cutar kanjamau, inda a ko da yaushe take tsaye a sahun gaba, don kula da masu fama da ciwon. Tana ta yin amfani da kwarewarta ta likitanci, da kulawa da take nunawa, don kawar da son zuciya, da tsoron da mutane ke da shi game da cutar kanjamau, ta kuma shigar da kuzari, da kyakkyawan fata ga mutane masu fama da ciwon kanjamau da ke cikin mawuyacin hali. Har ma ta zama abin koyi a fagen yaki da cutar kanjamau a kasar ta Sin.
15-Apr-2026
A yayin da rikice-rikice da rashin zaman lafiya ke ci gaba da ci wa ba wai kasashen yankin ba har ma da sauran sassan duniya tuwo a kwarya, kasar Sin na kara daukar matakin shiga cikin harkokin diflomasiyya domin hada karfi da karfe wajen maido da zaman lafiya. Kwanan nan, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gana da Sheikh Khaled bin Mohamed bin Zayed, yarima mai jiran gado na masarautar na Abu Dhabi ta Hadaddaiyar Daular Larabawa (UAE), a nan birnin Beijing. A yayin tattaunawarsu, firaminista Li ya sake tabbatar da shirin kasar Sin na taka rawar gani wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Gulf.
15-Apr-2026
Imrana Salisu, dan garin Zariya ne daga jihar Kadunan Najeriya, wanda a yanzu haka yake karatun digiri na uku a fannin injiniyancin tsaftace muhalli a wata jami’a mai suna UCAS a takaice a nan birnin Beijing na kasar Sin. A zantawarsa da Murtala Zhang, malam Imrana Salisu wanda ya samu digiri na biyu ma a nan kasar Sin, ya bayyana wasu abubuwan ci gaba da suka burge shi a kasar...
14-Apr-2026