04-Feb-2026
04-Feb-2026
31-Jan-2026
30-Jan-2026
29-Jan-2026
28-Jan-2026
27-Jan-2026
26-Jan-2026
Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin da Jamhuriyar Tarayyar Najeriya sun kulla dangantakar diflomasiyya a ranar 10 ga watan Fabrairun shekara ta 1971, inda a bana ne wato shekara ta 2026, ake cika shekaru 55 da kulla dangantakar diflomasiyya tsakaninsu. A cikin wadannan shekaru, dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu ta bunkasa cikin sauri, musamman a fannonin hadin gwiwa da suka shafi gina muhimman ababen more rayuwa, da raya harkokin tattalin arziki da kasuwanci, da bunkasa ayyukan gona, da kuma kara mu’amalar al’adu da cudanyar al’umma. Tun daga shirinmu na wannan sati, za mu gabatar muku da wasu jerin shirye-shirye guda hudu masu lakabin “Kabakin Arziki”, game da nasarorin da aka samu wajen karfafa hadin gwiwa da mu’amala tsakanin Sin da Najeriya...
03-Feb-2026
03-Feb-2026
A gundumar Chaihu dake garin Zhongxiang na lardin Hubei na tsakiyar kasar Sin, wata matashiya na duke sanye da malafa, tana duba yanayin karas din da ta shuka. Wace ce wannan matashiya? Sunan ta Tian Yu’ai, mai karatun digiri na 2 ta yanke shawarar komawa garinsu bayan kammala jami’a. An haife ta ne a shekarun 1990, kuma ita ce shugabar kungiyar gama kai ta manoman kayan lambu ta Zhongxiang Maotai. Ta shafe shekaru 8 da suka gabata tana raya aikin noman karas a kauyensu. A farkon shekarar 2025 aka karrama ta da lambar yabo ta abar koyi ta kasa.
02-Feb-2026
01-Feb-2026