20-Apr-2026
20-Apr-2026
20-Apr-2026
17-Apr-2026
16-Apr-2026
16-Apr-2026
15-Apr-2026
14-Apr-2026
A karshen shekarar 2023, wasu daliban kasar Kenya da suke karatu a jami’ar Jiaotong ta Beijing wato BJTU, da ma wasu da suka riga suka kammala karatu daga jami’ar, suka rubutawa shugaban kasar Sin Xi Jinping wasika, ina suka bayyana matukar jin dadin zuwansu kasar Sin, domin koyon ilimin sarrafawa da tafiyar da harkokin kulawa da layin dogo. Sun kuma bayyana fatan zama gadar abota tsakanin Sin da Kenya. A watan Janairun 2024, shugaba Xi Jinping ya ba su amsa wasikar, inda ya karfafa musu gwiwar ci gaba da bayar da gudunmuwa ga raya abotar da ke tsakanin Sin da Kenya da kuma wadda ke tsakanin Sin da Afrika.
20-Apr-2026
Yayin da gasar cin kofin kwallon kafa na duniya wadda hukumar FIFA ke shiryawa take kara karatowa, ita ma gasar kwallon kafa ta ‘yan wasa da ba kwararru ba ta kasar Sin, ko "Su Super League", ta yi matukar jan hankalin sassan duniya. ‘Yan wasa masu fafatawa a gasar, da ‘yan kallo na ta halartar filayen wasa domin nishadantuwa daga wannan gasa mai samun karin farin jini. Yayin da a gefe guda gasar ta "Su Super League" ke kara fadada sayayya, da hada-hadar kasuwanci a yankunan da ake gudanar da ita.
16-Apr-2026
A watan Maris na shekara ta 2026, wata likita 'yar kasar Sin daga birnin Nanchang na lardin Jiangxi dake kudu maso gabashin kasar mai suna Hu Minhua, wadda ta kware a fagen yaki da cutar kanjamau, ta samu lambar yabo ta fitacciyar mace ta kasa. Hu Minhua, ta shafe shekaru 26 tana jajircewa a fannin kandagarki da maganin cutar kanjamau, inda a ko da yaushe take tsaye a sahun gaba, don kula da masu fama da ciwon. Tana ta yin amfani da kwarewarta ta likitanci, da kulawa da take nunawa, don kawar da son zuciya, da tsoron da mutane ke da shi game da cutar kanjamau, ta kuma shigar da kuzari, da kyakkyawan fata ga mutane masu fama da ciwon kanjamau da ke cikin mawuyacin hali. Har ma ta zama abin koyi a fagen yaki da cutar kanjamau a kasar ta Sin.
15-Apr-2026
A yayin da rikice-rikice da rashin zaman lafiya ke ci gaba da ci wa ba wai kasashen yankin ba har ma da sauran sassan duniya tuwo a kwarya, kasar Sin na kara daukar matakin shiga cikin harkokin diflomasiyya domin hada karfi da karfe wajen maido da zaman lafiya. Kwanan nan, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gana da Sheikh Khaled bin Mohamed bin Zayed, yarima mai jiran gado na masarautar na Abu Dhabi ta Hadaddaiyar Daular Larabawa (UAE), a nan birnin Beijing. A yayin tattaunawarsu, firaminista Li ya sake tabbatar da shirin kasar Sin na taka rawar gani wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Gulf.
15-Apr-2026