14-May-2026
14-May-2026
13-May-2026
12-May-2026
09-May-2026
07-May-2026
07-May-2026
06-May-2026
Dan wasan kwallon Snooker na kasar Sin Wu Yize, ya haska sosai a gasar kasa da kasa da aka buga a filin wasa na Sheffield dake South Yorkshire na kasar Ingila, inda a wasan karshe na farkon makon jiya, ya yi nasarar doke abokin karawarsa Shaun Murphy na Ingila da ci 18 da 17.
14-May-2026
A matsayin muhimman membobi kasashe masu tasowa a duniya, Sin da kasashen Afirka suna karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, inda ba samar da karsashin “kara sauri” ga juna da samun zamanantarwa tare kawai suke yi ba, har ma za su jagoranci sana’ar zamanantarwa ta dukkanin kasashe masu tasowa. A cikin shirin mu na yau, bari mu ji ra’ayoyin wasu jami’an gwamnati da kwararru da masana guda hudu daga Sin da kasashen Afirka, mu waiwayi yadda Sin da Afirka suke inganta zamanantarwa a tarihinsu, da kuma sakamakon hadin gwiwa da suka samu, tare da bayyana ma’anarsu mai zurfi ga duniya.
13-May-2026
A yanzu haka dai, hankalin duniya ya karkata zuwa kasar Sin inda shugaban kasar Xi Jinping yake karbar bakuncin shugaban Amurka Donald Trump, wanda masana harkokin siyasa da diflomasiyya da dama ke bayyanawa a matsayin babbar muhimmiyar ganawar diflomasiyya a wannan shekara. A daidai lokacin da yake-yake, rashin tabbas a tattalin arziki, takun-sakar kasuwanci, da rarrabuwar kawuna a siyasar duniya ke ci gaba da girgiza amincewa da juna a tsakanin kasashe, ana kallon wannan ziyara mai muhimmanci a matsayin fiye da wata ganawar shugabanni ta yau da kullum. Wata jarabawa ce da ake fatan ganin manyan kasashe biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya za su iya samun maslaha ta bai-daya a wannan zamani mai cike da rashin tabbas.
13-May-2026
Shirin nazarin kimiyya da fasaha na Sin da Afrika, shiri ne na kasa da kasa da jami’ar nazarin aikin gona ta Sin ta kaddamar a 2019. Ta hanyar hada kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da samar da masu basira, shirin na samar da ilimin kimiyya da fasaha da ke bayar da gudunmuwa ga ci gaban ayyukan gona a Afrika. An gabatar da dabarun kasar Sin da suka yi nasara ga sassan duniya, musamman wadanda ke da alaka da zamanantar da rayuwar kananan iyalai manoma, ta hanyar wannan shiri. Baya ga haka, an karfafa hadin gwiwar Sin da Afrika da musayar al’adu tsakaninsu. Margaret Simisi, daliba ce daga kasar Malawi, wadda ke zaman mai bincike a shirin, kuma ta bayyana jajircewarta wajen koyon dabarun aikin gona, wadanda za su taimaka wajen raya kasarta.
12-May-2026