19-Mar-2026
19-Mar-2026
18-Mar-2026
18-Mar-2026
18-Mar-2026
16-Mar-2026
12-Mar-2026
11-Mar-2026
Babban kocin kungiyar kwallon kafa ta kasar Brazil Carlo Ancelotti, ya ce tauraron kwallon kafa dan kasar Brazil Neymar da Silva Santos Júnior, ba ya cikin jerin ‘yan wasa da za su bugawa Brazil wasannin sada zumunta da kasahen Faransa da Croatia, duk da kasancewar wasannin biyu, za su baiwa kocin damar gwada ‘yan wasansa gabanin tantancewar karshe, kafin bude gasar cin kofin kwallon kafa ta duniya dake tafe nan da ‘yan watanni.
19-Mar-2026
Sabbin bayanai daga hukumar kididdiga ta kasar Sin sun nuna cewa, manyan ma’aunan tattalin arzikin kasar sun nuna an samu ci gaba mai karfi a cikin watanni biyu na farkon bana. Misali, samar da kayayyakin masana’antu ya karu da kashi 6.3 cikin 100 idan aka kwatanta da makamancin lokaci a bara, lamarin da ke nuna cewa masana’antu suna ci gaba da habaka tare da samun sabon kuzari. Haka kuma bangaren ayyukan hidima, wanda ya hada da harkokin yawon bude ido, nishadi da sauran hidimomi, ya karu da kashi 5.2 cikin 100, musamman bayan bukukuwan sabuwar shekarar gargajiya ta Sinawa wanda lokaci ne da ake samun karuwar kashe kudaden jama’a. A bangaren kasuwancin cikin gida kuma, sayar da kayayyakin masarufi ya karu da kashi 2.8 cikin 100, wanda ya nuna alamun karuwar sayayya a tsakanin al’umma.
18-Mar-2026
Ahmad Muhammad Nahannu, dan Kano ne wanda ya yi karatu tun daga digiri na farko har zuwa na uku a birane daban-daban na kasar Sin. A zantawarsa da Murtala Zhang, Ahmad Muhammad Nahannu wanda a yanzu haka ke karatun digiri na uku a fannin tsaron motoci masu amfani da na’ura mai kwakwalwa wato cybersecurity in intelligent connected vehicles a turance a wata jami’a da ke birnin Chongqing na kasar Sin, ya bayyana ra’ayinsa kan bambancin yanayin karatu da ke tsakanin kasar Sin da Najeriya, da fahimtarsa game da ci gaban kasar Sin, musamman a birnin Chongqing, gami da burin da yake son cimmawa bayan ya kammala karatu a nan kasar...
17-Mar-2026
Wang Miaoli, wata jami’ar ‘yan sanda mai shekaru 47, da ke kula da harkokin gudanar da shari’a da gyara halin masu shan kwayoyi a kasar Sin, ta jawo hankulan al’ummar kasar kwanan nan, saboda ta dakatar da masu kai harin wuka a kan titin. Abin da ba a sani ba shi ne, cikin shekaru 23 da suka gabata, ta yi aiki a sashen ilmantarwa na wani gidan gyaran halin masu shan miyagun kwayoyi da ke lardin Henan a tsakiyar kasar Sin, inda ta dage wajen yaki da miyagun kwayoyi, kuma ta taimakawa mutane masu yawa bisa jajircewa da sauke hakkin da ke wuyanta......
16-Mar-2026