29-May-2026
28-May-2026
27-May-2026
26-May-2026
26-May-2026
25-May-2026
21-May-2026
20-May-2026
A yankin arewa maso gabashin kasar Sin inda yanayin hunturu kan kai maki 30 kasa da sufuli, kuma wuri da tattalin arzikinsa ya sha fama da kalubale cikin shekaru masu yawa, a yanzu yankin ya tsunduma cikin yanayi na nishadi. Inda a ranar Asabar din karshen makon jiya, aka kaddamar da gasar kwallon kafa ajin ‘yan wasa da ba kwararru ba, wadda aka yiwa lakabi da “Northeast Super League”.
28-May-2026
A baya bayan nan gwamnatin kasar Sin ta shirya kashe makudan kudade domin aiwatar da wata manufa da aka yiwa lakabi da “Hadaddun tsare-tsare shida” ko "Six Networks" a Turance. Wato wata manufa ta bunkasa dinke fannonin ababen more rayuwa guda shida, domin biyan sabbin bukatun al’ummar kasar, da kuma wanzar da ci gaban tattalin arzikinta mai inganci. Manufar “Hadaddun tsare-tsare shida” ta kunshi kara inganta tsarin cin gajiyar ruwa, wanda karkashin hakan za a gudanar da karin ayyukan karkata ruwa zuwa wuraren bukatarsa, da amfani da shi wajen ban ruwa ko noman rani, da kare ambaliya, da samar da issashen ruwa na amfanin yau da kullum na al’umma.
27-May-2026
Kwanan nan ne aka gudanar da taron dandalin tattaunawa na matasan kasar Sin masu nazarin batutuwan Afirka na shekarar 2026, mai taken “Koyi da juna a bangaren musanyar al’adu da jama’a tsakanin Sin da Afirka gami da samar da ilimi” a jami’ar koyon harsunan waje ta Beijijng, wato BFSU a takaice, dandalin da ya kasance wata muhimmiyar kafa ta murnar shekarar mu’amalar al’adu da cudanyar jama’a ta Sin da Afirka. Wasu matasan kasar Sin masu nazarin batutuwan Afirka da suka halarci dandalin a wannan karo, sun bayyana ra’ayoyinsu kan hadin gwiwar Sin da Afirka, da burin da suke son cimmawa bisa karatun da suke yi...
26-May-2026
25-May-2026