15-Jun-2026
13-Jun-2026
12-Jun-2026
11-Jun-2026
10-Jun-2026
05-Jun-2026
04-Jun-2026
03-Jun-2026
A makon da ya gabata, mun kawo muku labarin yadda kasar Sin ke kokarin kyautata tsarin nuna kauna da ba da kulawa da kariya ga yara, musamman ga wadanda suke cikin mawuyacin hali. Mun ga yadda ma’aikatan jinya a gidan jin dadin yara na birnin Yangzhou suke sadaukar da kansu wajen kula da marayu masu nakasa mai tsanani. Mun kuma lura cewa, gwamnatin Sin ta samar da tsarin manufofi masu karfi, tare da kara yawan tallafin kudi ga marayu da yara nakasassu. Bugu da kari, an aiwatar da shirin tiyata da gyaran jiki ga marayu nakasassu har sau 273,000, wanda ya dawo da begen rayuwa ga dimbin yara. Mun kuma ambaci cewa an rage yawan cibiyoyin jin dadin yara kuma an mayar da su cibiyoyin bude kofa ga al’umma.
15-Jun-2026
Yanzu haka dai ana gab da bude gasar cin kofin kwallon kafa na duniya na hukumar FIFA, kuma kasar Mexico za ta fafata da Afirka ta kudu a gasar ta bana a ranar 11 ga watan Yunin nan a filin wasa na birnin Mexico, inda kasashen biyu za su maimaita haduwarsu a makamanciyar wannan gasa ta shekarar 2010. A wannan karo, Afirka ta kudu ta sake dawowa wannan gasa a karon farko tun waccan gasa ta 2010.
11-Jun-2026
Har kullum ababen more rayuwa na taka rawar gani, wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasar Sin. Kuma hakan ne ma yasa mahukuntan kasar ke kara bullo da matakai daban daban na bunkasa fannin ciki har da bangaren sufuri. A karkashin hakan, a kwanan nan gwamnatin Sin ta kaddamar da wani katafaren aikin samar da hanyar sufurin ruwa, a kan kogi na uku mafi tsayi a duniya wato kogin Yangtze, wanda kuma shi ne kogi mafi tsayi a dukkanin fadin nahiyar Asiya. Tsayin kogin Yangtze ya kai kilomita 6,300. Yana kuma gudana baki daya a cikin sassan kasar, tun daga tsaunin Tibet zuwa yankin tekun gabashin kasar kusa da birnin Shanghai.
10-Jun-2026
Sadiq Muhammad Miji, dan asalin Gombe ne daga tarayyar Najeriya, wanda a yanzu haka yake karatun digiri na biyu a fannin ilimin zane-zanen gidaje wato architecture a turance a jami’ar koyon ilimin gandun daji ta Beijing ko kuma BFU a takaice. A zantawarsa da Murtala Zhang, malam Sadiq wanda ya shigo birnin Beijing tun shekara ta 2024, ya ce ya riga ya saba da yanayin rayuwa a nan kasar Sin, tare da bayyana abubuwan da suka burge shi matuka a nan kasar. Sadiq Muhammad Miji ya kuma bayyana burin da yake son cimmawa...
09-Jun-2026