14-Jan-2026
14-Jan-2026
13-Jan-2026
13-Jan-2026
11-Jan-2026
09-Jan-2026
08-Jan-2026
08-Jan-2026
A karshen shekarar da ta gabata, an fara gudanar da ayyuka daga dukkan fannoni don sake farfado da layin dogo da ya hada kasashen Tanzaniya da Zambiya. A cikin shirinmu na yau, za mu binciki yadda wannan “Hanyar Sada Zumunta” mai dauke da martabar tarihi yake rubuta sabon babi a cikin hadin-gwiwar Sin da Afirka tare da samun nasara.
14-Jan-2026
Shirin Duniyarmu A Yau na makon nan, ya mayar da hankali ne a kan wani muhimmin mataki da aka taka da zai kara karfafa goyon bayan al’umma ga abotar da ke tsakanin Sin da Afirka a wani sabon mafari na tarihi. Wannan muhimmin mataki ba wai kawai game da diflomasiyya ba ne, a’a, abu ne da ya shafi jama’a, da al'adu, da kuma burin da ake son cimmawa a kan turbarmu gudu tare, mu tsira tare. Shi ne wani shiri aka kaddamar na shekarar cudanyar jama’a da musayar al’adu a tsakanin Sin da Afirka a kwanan nan.
14-Jan-2026
Du Mengyuan na sarrafa injunan aikin gona a gundumar Lushan, dake birnin Pingdinshan na lardin Henan dake tsakiyar kasar Sin. A shekarar 2023, ta koma garinsu bayan ta kammala karatun jami’a. Bayan shekara daya kuma, ta samu lasisin tukin motar tarakta da ta girbi.
12-Jan-2026
An bude shekarar 2025 da gasar wasannin motsa jiki ta nahiyar asiya, wadda ta gudana tsakanin ranakun 7 zuwa 14 watan Fabarairun shekarar a birnin Harbin, gasar da ta hallara ‘yan wasa sama da 1,200 daga kasashe da yankunan duniya 34, ta kuma zamo mafi tara yawan ‘yan wasan motsa jiki a tarihinta. Kasar Sin ce ta zamo ta daya a fannin samun lambobin yabo a gasar, inda ‘yan wasanta suka lashe lambobin zinari 32, da na azurfa 27 da kuma na tagulla 26, kana ‘yan wasan Sin daga Taipei da na kasar Thailand, su ma suna kan gaba wajen cimma manyan nasarori a gasar.
08-Jan-2026