06-May-2026
01-May-2026
30-Apr-2026
29-Apr-2026
29-Apr-2026
23-Apr-2026
23-Apr-2026
22-Apr-2026
Shirin Duniyarmu A Yau na wannan makon, ya duba wani batu mai matukar muhimmanci ga dorewar rayuwar al’ummar duk duniya cikin aminci, shi ne abin da ya shafi bukatar karfafa matakan rigakafin bala’o’i daga indallahi tun kafin su abku. Gaskiya ne cewa, komai mukaddari ne, amma kuma Allah ya yi wa dan’adam hankali da ilimi domin ya kula da tsarin rayuwarsa ta yadda zai fahimci abin da zai cutar da shi ya guje masa, ya kuma gane abin da zai amfane shi don ya rungume shi. Shi ya sa ma Hausawa ke cewa, “Taya Allah kiwo, ya fi Allah na nan.”
06-May-2026
Ga ragowar hirar da Murtala Zhang ya yi da Muktar Abubakar Bagudo, dan asalin jihar Kebbin Najeriya, wanda a yanzu haka ke karatun digiri na biyu a fannin kasuwanci a jami’ar kasuwanci da tattalin arzikin kasa da kasa wato UIBE a takaice da ke birnin Beijing na kasar Sin, inda ya kara bayyana wasu abubuwan da suka burge shi, sakamakon ziyarar da ya yi a wurare daban-daban na kasar Sin, tare da bayyana fatansa da kira na musamman ga ’yan Najeriya...
05-May-2026
Masu sauraro, a makon da ya wuce, mun gabatar muku labari game da Wang Zhuolun, ’yar jaridar kasar Sin dake aiki a yankin Kudus, wadda ba ta ji tsoron hadari ba ta garzaya zuwa fagen yaki bayan barkewar rikicin Falasdinu da Isra'ila a shekarar 2023, a daidai lokacin da kafofin yada labarai na duniya suka fice daga yankin, ta tsaya kyam a bakin aikinta, inda ta yi amfani da kwarewa, jajircewa da lamiri na ’yar jaridar Sin, don rubuta ainihin tarihi da bayyana gaskiya ta hanyar kalmomi da kyamarori. A bayan irin wannan tsayin daka, akwai kwarewarta da kuma burinta na asali a matsayinta na ’yar jarida. Ta yaya Wang Zhuolun take kokarin bayar da rahoto na gaggawa da kuma nuna karfin fada-a-ji? Kuma ta yaya ta bayyana hasken zaman lafiya a tsakanin hayakin yaki? A cikin shirinmu na yau za mu ci gaba da kawo muku labari ne game da wannan baiwar Allah.
04-May-2026
Shahararriyar ‘yar wasan kwallon tebur ‘yar kasar Sin, wadda kuma ta taba lashe gasar Olympic, da gasar cin kofin duniya na wasan Liu Shiwen, ta ce har yanzu tana sha’awar ci gaba da fafatawa a fannin wannan wasa, duk da shafe shekaru hudu ba tare da shiga gasannin kasa da kasa ba.
30-Apr-2026