20-Aug-2026
20-Aug-2026
19-Aug-2026
17-Aug-2026
15-Aug-2026
13-Aug-2026
13-Aug-2026
12-Aug-2026
A halin yanzu al’ummun kasar Sin na kara mayar da hankali ga sha’anin wasanni, fannin da baya ga nishadantarwa a shekarun baya bayan nan ke kara samar da damarmaki na bunkasa samar da kudaden shiga.
20-Aug-2026
Shirin Duniyarmu A Yau na wannan makon ya mayar da hankali ne a kan wasu muhimman batutuwa guda biyu, na farko shi ne yanayin tattalin arzikin kasar Sin a watan Yuli, wanda ya nuna juriya da kuzari duk da kalubalen yanayi na rashin tabbas a duniya. Na biyu kuma shi ne game da wani shiri mai ban sha’awa da gwamnatin Sin ta fito da shi wanda a karkashi aka dauki sabbin matakai na musamman don bunkasa sayayya ko cefane a kananan hukomomi da garuruwa har ma da karkara, inda wannan mataki ko tantamu babu zai kara wa tattalin arzikin cikin gida tagomashi da kuma kara fadada cin gajiyar arzikin kasa a lunguna da sako na kasar Sin.
19-Aug-2026
Dr. Musa Abubakar Tadda, dan asalin jihar Kano ne a tarayyar Najeriya kuma mai bincike mai zurfi a fannin fasahar noma, inganta muhalli, da kuma makamashi a birnin Hangzhou na lardin Zhejiang da ke gabashin kasar Sin. A zantawarsa da Murtala Zhang, Dr. Musa Tadda wanda ya shigo kasar Sin tun shekara ta 2017, ya bayyana ra’ayinsa kan yanayin rayuwa da karatu a kasar Sin, da kuma burin da yake son cimmawa bisa karatun da ya yi a kasar...
18-Aug-2026
17-Aug-2026