19-Aug-2026
17-Aug-2026
15-Aug-2026
13-Aug-2026
13-Aug-2026
12-Aug-2026
10-Aug-2026
09-Aug-2026
Shirin Duniyarmu A Yau na wannan makon ya mayar da hankali ne a kan wasu muhimman batutuwa guda biyu, na farko shi ne yanayin tattalin arzikin kasar Sin a watan Yuli, wanda ya nuna juriya da kuzari duk da kalubalen yanayi na rashin tabbas a duniya. Na biyu kuma shi ne game da wani shiri mai ban sha’awa da gwamnatin Sin ta fito da shi wanda a karkashi aka dauki sabbin matakai na musamman don bunkasa sayayya ko cefane a kananan hukomomi da garuruwa har ma da karkara, inda wannan mataki ko tantamu babu zai kara wa tattalin arzikin cikin gida tagomashi da kuma kara fadada cin gajiyar arzikin kasa a lunguna da sako na kasar Sin.
19-Aug-2026
Dr. Musa Abubakar Tadda, dan asalin jihar Kano ne a tarayyar Najeriya kuma mai bincike mai zurfi a fannin fasahar noma, inganta muhalli, da kuma makamashi a birnin Hangzhou na lardin Zhejiang da ke gabashin kasar Sin. A zantawarsa da Murtala Zhang, Dr. Musa Tadda wanda ya shigo kasar Sin tun shekara ta 2017, ya bayyana ra’ayinsa kan yanayin rayuwa da karatu a kasar Sin, da kuma burin da yake son cimmawa bisa karatun da ya yi a kasar...
18-Aug-2026
17-Aug-2026
A cikin shirinmu da ya gabata, mun saka muku hirar da wakiliyarmu Fa’iza Muhammad Mustapha ta yi da sabon jakadan Najeriya a kasar Sin, Abdulrahman Dambazau, game da nasarorin da aka samu a hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Najeriya tun bayan kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu. Kuma a cikin shirinmu na wannan mako, za mu saka muku ragowar tattaunawarsu, wadda ta shafi wasu fannoni uku, wato musayar al’adu da cudanyar jama’a, da kuma fa’idojin manufofin Sin ga Afirka, gami da tsare-tsaren ci gaban kasashen biyu da kuma makomar hadin gwiwarsu a nan gaba, musamman ma kan ci gaban abokantaka tsakanin Sin da Najeriya.
12-Aug-2026