12-Aug-2026
10-Aug-2026
09-Aug-2026
07-Aug-2026
06-Aug-2026
06-Aug-2026
05-Aug-2026
03-Aug-2026
A cikin shirinmu da ya gabata, mun saka muku hirar da wakiliyarmu Fa’iza Muhammad Mustapha ta yi da sabon jakadan Najeriya a kasar Sin, Abdulrahman Dambazau, game da nasarorin da aka samu a hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Najeriya tun bayan kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu. Kuma a cikin shirinmu na wannan mako, za mu saka muku ragowar tattaunawarsu, wadda ta shafi wasu fannoni uku, wato musayar al’adu da cudanyar jama’a, da kuma fa’idojin manufofin Sin ga Afirka, gami da tsare-tsaren ci gaban kasashen biyu da kuma makomar hadin gwiwarsu a nan gaba, musamman ma kan ci gaban abokantaka tsakanin Sin da Najeriya.
12-Aug-2026
Shirin Duniyarmu A Yau na wannan karo ya dau harama ne daga wani tsohon karin magana na Sinanci da yake cewa, “Shin ba abin farin ciki ba ne a sami abokai suna zuwa ziyararka daga nesa?” Wannan kyakkyawar magana tana nuna farin cikin karbar baki, da gina amincewa, da karfafa dangantaka. Sannan, baya ga abota tsakanin mutane, hikimar wannan karin magana tana kuma bayyana yadda kasashe ke hulda da juna ta hanyar diflomasiyya, da tattaunawa da kuma kulla hadin gwiwa domin samun ci gaba.
12-Aug-2026
“Na zo Chengdu don ganin manyan dabbobin Panda, kuma sai na zauna saboda mutanen birnin da kuma harkokin wasanni,” cewar Lamia Arab wadda ta zo Sin daga birnin London na Birtaniya. Ta je Chengdu, babban birnin lardin Sichuan ne a 2017. Yanzu malama ce a jami’ar Chengdu. Wasanni sun zama tamkar fasfonta yayin zama a Chengdu, al’ada kuma ta zama abun da ya zaunar da ita a birnin. A ganinta, Chengdu ba waje ne mai hada-hada ba kadai, misali ne na wurin da ya hada wasanni da al’adu, kuma inda gargajiya da zamani suka hade da juna.
10-Aug-2026
09-Aug-2026