20-Apr-2026
20-Apr-2026
20-Apr-2026
17-Apr-2026
16-Apr-2026
16-Apr-2026
15-Apr-2026
14-Apr-2026
A ’yan shekarun baya bayan nan, sassan kasar Sin daban daban na ta kara mayar da hankali ga bunkasa tattalin arzikin kasar ta hanyar kirkiro sabbin fasahohin zamani. Cikin sassan kasar da suka yi fice a wannan fage akwai manyan lardunanta guda 10, wadanda aka yi amannar suna kara azamar amfani da fifikon tattalin arzikinsu, wajen bunkasa fannin kirkire-kirkire da kere-keren zamani, domin ingiza ci gaba mai inganci na kasar baki daya. Alkaluma sun shaida yadda manyan lardunan kasar Sin 10, ciki har da lardunan Guangdong da Jiangsu da Shandong da kuma birnin Shanghai, suke samar da gudummawar sama da kaso 60 bisa dari na daukacin ma’aunin tattalin arziki na GDPn kasar Sin, duk da cewa fadin wadannan yankunan bai kai daya bisa biyar na daukacin fadin yankin kasar ba.
22-Apr-2026
Tun da safiya, jirgin kasa dake tafiya a kan layin dogo mai fadin mita daya yana isowa kan lokaci tashar jiragen kasa ta Mombasa dake kasar Kenya. Ga mazauna yankin, wannan jirgin kasa “damar kara sauri” ce game da zirga-zirgarsu ta yau da kullum. A cikin shirinmu na yau, zan gabatar muku labarin yadda kamfanin Sin ya taimaka wajen farfado da layin dogo a Kenya.
21-Apr-2026
A karshen shekarar 2023, wasu daliban kasar Kenya da suke karatu a jami’ar Jiaotong ta Beijing wato BJTU, da ma wasu da suka riga suka kammala karatu daga jami’ar, suka rubutawa shugaban kasar Sin Xi Jinping wasika, ina suka bayyana matukar jin dadin zuwansu kasar Sin, domin koyon ilimin sarrafawa da tafiyar da harkokin kulawa da layin dogo. Sun kuma bayyana fatan zama gadar abota tsakanin Sin da Kenya. A watan Janairun 2024, shugaba Xi Jinping ya ba su amsa wasikar, inda ya karfafa musu gwiwar ci gaba da bayar da gudunmuwa ga raya abotar da ke tsakanin Sin da Kenya da kuma wadda ke tsakanin Sin da Afrika.
20-Apr-2026
Yayin da gasar cin kofin kwallon kafa na duniya wadda hukumar FIFA ke shiryawa take kara karatowa, ita ma gasar kwallon kafa ta ‘yan wasa da ba kwararru ba ta kasar Sin, ko "Su Super League", ta yi matukar jan hankalin sassan duniya. ‘Yan wasa masu fafatawa a gasar, da ‘yan kallo na ta halartar filayen wasa domin nishadantuwa daga wannan gasa mai samun karin farin jini. Yayin da a gefe guda gasar ta "Su Super League" ke kara fadada sayayya, da hada-hadar kasuwanci a yankunan da ake gudanar da ita.
16-Apr-2026