03-Aug-2026
03-Aug-2026
30-Jul-2026
29-Jul-2026
27-Jul-2026
24-Jul-2026
24-Jul-2026
24-Jul-2026
Kwanan nan, wakiliyarmu Fa’iza Muhammad Mustapha ta yi wata hira ta musamman da sabon jakadan Najeriya a kasar Sin, Abdulrahman Dambazau. A cikin shirinmu na yau, bari mu waiwayi nasarorin da aka samu a hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Najeriya tun bayan kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu, a cikin hirar wakiliyarmu da jakada Dambazau.
05-Aug-2026
Daga masu yawon bude ido da ke ziyartar Sin zuwa ga bakin kasashen waje da suka zabi zama, karatu ko aiki a kasar, mutane da dama suna sauyawa daga zuwa su kalli kasar Sin kawai zuwa fahimtar al’adunta da kuma gwada amfani da wasu daga cikin tsare-tsaren rayuwarta a rayuwarsu ta yau da kullum, inda hakan ke kara habaka kyakkyawar fahimtar da ake wa kasar a fadin duniya, kamar dai yadda a kwanan nan rahoton binciken da Cibiyar Pew ta gudanar ya nuna.
05-Aug-2026
04-Aug-2026
Lin Donghong, wadda ta fito daga lardin Guangdong a kudancin kasar Sin, ta kwashe sama da shekaru ashirin tana gogayya a harkar sufurin jiragen sama da yawon bude ido da al'adu. Ta dade tana aiki a Kamfanin Jiragen Sama na China Southern, inda ta zurfafa saninta a fannin hidimar yawon bude ido, sannan daga baya ta tsunduma cikin harkar yawon bude ido da al'adu ta kasa da kasa. A shekarar 2018, ta shiga Fliggy, dandalin balaguro na kamfanin Alibaba, inda ta ci gaba da tuntubar ayyukan yawon bude ido da al’adu na cikin gida da na kasashen waje. Ta shafe shekaru tana zirga-zirga tsakanin manyan biranen gida da waje da yawa, abin da ya ba ta damar yin hangen nesa mai fadi a duniya. Bayan aiki, ta kan dauki nauyin ayyukan agaji. Yayin da take tattaunawa da ma’aikatan dake aiki a sahun gaba na kauyuka, sannu a hankali ta fara samun ra’ayin tsunduma cikin al’amuran karkara, da bayar da gudummawa wajen raya kauyuka.
03-Aug-2026