29-Apr-2026
29-Apr-2026
28-Apr-2026
28-Apr-2026
28-Apr-2026
27-Apr-2026
27-Apr-2026
27-Apr-2026
Shirin Duniyarmu A Yau, ya mayar da hankali ne kan gawurtaccen bikin baje kolin kasuwancin nan na duniya wato Canton Fair na kasar Sin wanda na bana shi ne karo na 139, da ake gudanarwa a birnin Guangzhou na kasar Sin. Wannan baje koli ya sake nuna muhimmancinsa a matsayin babban dandali na kasuwanci tsakanin kasashe, inda ya jawo hankulan masu sayayya da masu sayarwa daga kasashen waje har guda 245,000 daga kasashe da yankuna 219 a zangonsa na farko da aka ci sau biyu kacal.
29-Apr-2026
Muktar Abubakar Bagudo, dan asalin jihar Kebbin Najeriya ne, wanda a yanzu haka ke karatun digiri na biyu a fannin kasuwanci a jami’ar kasuwanci da tattalin arzikin kasa da kasa wato UIBE a takaice da ke birnin Beijing na kasar Sin. A zantawarsa da Murtala Zhang, malam Muktar Abubabar Bagudo ya bayyana ra’ayinsa kan yanayin karatu a kasar Sin, da yadda Najeriya da Sin za su yi koyi da juna, duba da kamanceceniya da ke akwai tsakaninsu, da sauran wasu abubuwa da dama da ya ce, shi ganau ne ba jiyau ba...
28-Apr-2026
28-Apr-2026
Kudus, “Birni Mai Tsarki” ya kasance wurin girmama addinai na tsawon shekaru dubu ga Yahudawa, Kiristoci da kuma Musulmai, kullum yana fama da rikice-rikice, kuma ko da yaushe yana kan gaba a duniya a batutuwan da kafafen yada labarai suka fi mayar da hankali akai. A cikin wannan yanki mai cike da rashin tabbas, ba a taba rasa ’yan jaridar kasar Sin ba. A watan Fabrairun shekara ta 2022, Wang Zhuolun mai shekara 32 ta isa birnin, inda ta zama babbar wakiliyar Kamfanin Dillancin Labarai na Xinhua da ke birnin na Kudus. A matsayinta na daya daga cikin ’yan jaridun Sin da suka fi dadewa wajen aiki a yankuna masu fama da rikici tsakanin Isra’ila da Falasdinu, ta yi amfani da kwarewa, jajircewa da lamiri na ‘yar jaridar Sin, don rubuta ainihin tarihi da bayyana gaskiya ta hanyar kalmomi da kyamarori. Ta isar wa duniya muryar Sin mai mara nuna bangaranci, cike da tausayi irin na bil’adama. Haka kuma, ta idanunta ta sa al’ummar duniya sun fahimci wahalhalun da mazauna yankin ke sha da begensu
27-Apr-2026